The Quran in Hausa - Surah Duha translated into Hausa, Surah Ad-Dhuha in Hausa. We provide accurate translation of Surah Duha in Hausa - الهوسا, Verses 11 - Surah Number 93 - Page 596.

| وَالضُّحَىٰ (1) Inã rantsuwa da hantsi | 
| وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَىٰ (2) Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa) | 
| مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ (3) Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba | 
| وَلَلْآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الْأُولَىٰ (4) Kuma lalle ta ƙarshe* ce mafi alheri a gare ka daga ta farko | 
| وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىٰ (5) Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda | 
| أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَىٰ (6) Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma | 
| وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَىٰ (7) Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai | 
| وَوَجَدَكَ عَائِلًا فَأَغْنَىٰ (8) Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka | 
| فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلَا تَقْهَرْ (9) Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi | 
| وَأَمَّا السَّائِلَ فَلَا تَنْهَرْ (10) Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa | 
| وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْ (11) Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya) |