Quran with Hausa translation - Surah Ar-Ra‘d ayat 31 - الرَّعد - Page - Juz 13
﴿وَلَوۡ أَنَّ قُرۡءَانٗا سُيِّرَتۡ بِهِ ٱلۡجِبَالُ أَوۡ قُطِّعَتۡ بِهِ ٱلۡأَرۡضُ أَوۡ كُلِّمَ بِهِ ٱلۡمَوۡتَىٰۗ بَل لِّلَّهِ ٱلۡأَمۡرُ جَمِيعًاۗ أَفَلَمۡ يَاْيۡـَٔسِ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَن لَّوۡ يَشَآءُ ٱللَّهُ لَهَدَى ٱلنَّاسَ جَمِيعٗاۗ وَلَا يَزَالُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ تُصِيبُهُم بِمَا صَنَعُواْ قَارِعَةٌ أَوۡ تَحُلُّ قَرِيبٗا مِّن دَارِهِمۡ حَتَّىٰ يَأۡتِيَ وَعۡدُ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُخۡلِفُ ٱلۡمِيعَادَ ﴾
[الرَّعد: 31]
﴿ولو أن قرآنا سيرت به الجبال أو قطعت به الأرض أو كلم﴾ [الرَّعد: 31]
Abubakar Mahmood Jummi Kuma da lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwatsu game da shi, ko kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (da ba su yi imani ba). A'a ga Allah al'amari yake gaba ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi imani ba su yanke tsammani ba da cewa da Allah Ya so, da Ya shiryar da mutane gaba ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kafirci ba za su gushe ba wata masifa tana samun su saboda abin da suka aikata, ko kuwa ka sauka* kusa da gidajensu, har wa'adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah ba ya saɓa wa lokacin alkawari |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma da lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwatsu game da shi, ko kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (da ba su yi imani ba). A'a ga Allah al'amari yake gaba ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi imani ba su yanke tsammani ba da cewa da Allah Ya so, da Ya shiryar da mutane gaba ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kafirci ba za su gushe ba wata masifa tana samun su saboda abin da suka aikata, ko kuwa ka sauka kusa da gidajensu, har wa'adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah ba ya saɓa wa lokacin alkawari |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma dã lalle an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwãtsu game da shi, kõ kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi (dã ba su yi ĩmãni ba). Ã'a ga Allah al'amari yake gabã ɗaya! Shin fa, waɗanda suka yi ĩmãni ba su yanke tsammãni ba da cẽwa da Allah Yã so, dã Yã shiryar da mutãne gabã ɗaya? Kuma waɗanda suka yi kãfirci ba zã su gushe ba wata masĩfa tanã samun su sabõda abin da suka aikata, kõ kuwa ka saukã kusa da gidãjẽnsu, har wa'adin Allah ya zo. Kuma lalle ne Allah bã ya sãɓã wa lõkacin alkawari |