Quran with Hausa translation - Surah Al-Fath ayat 29 - الفَتح - Page - Juz 26
﴿مُّحَمَّدٞ رَّسُولُ ٱللَّهِۚ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥٓ أَشِدَّآءُ عَلَى ٱلۡكُفَّارِ رُحَمَآءُ بَيۡنَهُمۡۖ تَرَىٰهُمۡ رُكَّعٗا سُجَّدٗا يَبۡتَغُونَ فَضۡلٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِضۡوَٰنٗاۖ سِيمَاهُمۡ فِي وُجُوهِهِم مِّنۡ أَثَرِ ٱلسُّجُودِۚ ذَٰلِكَ مَثَلُهُمۡ فِي ٱلتَّوۡرَىٰةِۚ وَمَثَلُهُمۡ فِي ٱلۡإِنجِيلِ كَزَرۡعٍ أَخۡرَجَ شَطۡـَٔهُۥ فَـَٔازَرَهُۥ فَٱسۡتَغۡلَظَ فَٱسۡتَوَىٰ عَلَىٰ سُوقِهِۦ يُعۡجِبُ ٱلزُّرَّاعَ لِيَغِيظَ بِهِمُ ٱلۡكُفَّارَۗ وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ مِنۡهُم مَّغۡفِرَةٗ وَأَجۡرًا عَظِيمَۢا ﴾
[الفَتح: 29]
﴿محمد رسول الله والذين معه أشداء على الكفار رحماء بينهم تراهم ركعا﴾ [الفَتح: 29]
Abubakar Mahmood Jummi Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, kana ganin su suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala* daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.** Wannan shi ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injila ita ce kamar tsiron shuka wanda ya fitar da reshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafafunsa, yana bayar da sha'awa ga masu shukar' domin (Allah) Ya fusatar da kafirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gafara da ijara mai girma |
Abubakar Mahmoud Gumi Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, kana ganin su suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda. Wannan shi ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injila ita ce kamar tsiron shuka wanda ya fitar da reshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafafunsa, yana bayar da sha'awa ga masu shukar' domin (Allah) Ya fusatar da kafirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gafara da ijara mai girma |
Abubakar Mahmoud Gumi Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da shi mãsu tsanani ne a kan kãfirai, mãsu rahama ne a tsakãninsu, kanã ganin su sunã mãsu rukũ'i mãsu sujada, sunã nẽman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alãmarsu tanã a cikin fuskõkinsu, daga kufan sujuda. Wannan shĩ ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injĩla ita ce kamar tsiron shũka wanda ya fitar da rẽshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafãfunsa, yanã bãyar da sha'awa ga mãsu shũkar' dõmin (Allah) Ya fusãtar da kãfirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gãfara da ijãra mai girma |