Quran with Hausa translation - Surah An-Nisa’ ayat 140 - النِّسَاء - Page - Juz 5
﴿وَقَدۡ نَزَّلَ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ أَنۡ إِذَا سَمِعۡتُمۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ يُكۡفَرُ بِهَا وَيُسۡتَهۡزَأُ بِهَا فَلَا تَقۡعُدُواْ مَعَهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦٓ إِنَّكُمۡ إِذٗا مِّثۡلُهُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ جَامِعُ ٱلۡمُنَٰفِقِينَ وَٱلۡكَٰفِرِينَ فِي جَهَنَّمَ جَمِيعًا ﴾
[النِّسَاء: 140]
﴿وقد نـزل عليكم في الكتاب أن إذا سمعتم آيات الله يكفر بها﴾ [النِّسَاء: 140]
Abubakar Mahmood Jummi Kuma lalle ne Ya sassaukar* muku a cikin Littafi cewa idan kun ji ayoyin Allah, ana kafirta da su, kuma ana izgili da su, to, kada ku zauna tare da su, sai sun shiga cikin wani labari. Lalle ne ku, a lokacin nan misalinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tara munafukai da kafirai ne a cikin Jahannama gaba ɗaya |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma lalle ne Ya sassaukar muku a cikin Littafi cewa idan kun ji ayoyin Allah, ana kafirta da su, kuma ana izgili da su, to, kada ku zauna tare da su, sai sun shiga cikin wani labari. Lalle ne ku, a lokacin nan misalinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tara munafukai da kafirai ne a cikin Jahannama gaba ɗaya |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma lalle ne Yã sassaukar muku a cikin Littãfi cẽwa idan kun ji ãyõyin Allah, anã kãfirta da su, kuma anã izgili da su, to, kada ku zauna tãre da sũ, sai sun shiga cikin wani lãbãri. Lalle ne kũ, a lõkacin nan misãlinsu kuke. Lalle ne, Allah Mai tãra munãfukai da kãfirai ne a cikin Jahannama gabã ɗaya |