Quran with Hausa translation - Surah Al-hajj ayat 36 - الحج - Page - Juz 17
﴿وَٱلۡبُدۡنَ جَعَلۡنَٰهَا لَكُم مِّن شَعَٰٓئِرِ ٱللَّهِ لَكُمۡ فِيهَا خَيۡرٞۖ فَٱذۡكُرُواْ ٱسۡمَ ٱللَّهِ عَلَيۡهَا صَوَآفَّۖ فَإِذَا وَجَبَتۡ جُنُوبُهَا فَكُلُواْ مِنۡهَا وَأَطۡعِمُواْ ٱلۡقَانِعَ وَٱلۡمُعۡتَرَّۚ كَذَٰلِكَ سَخَّرۡنَٰهَا لَكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ ﴾
[الحج: 36]
﴿والبدن جعلناها لكم من شعائر الله لكم فيها خير فاذكروا اسم الله﴾ [الحج: 36]
Abubakar Mahmood Jummi Kuma raƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibadojin Allah. Kuna da wani alheri babba a cikinsu. Sai ku ambaci sunan Allah a kansu suna tsaye* a kan ƙafafu uku. Sa'an nan idan sasanninsu suka faɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da mai wadar zuci da mai bara. Kamar haka Muka hore muku su, tsammaninku kuna godewa |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma raƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibadojin Allah. Kuna da wani alheri babba a cikinsu. Sai ku ambaci sunan Allah a kansu suna tsaye a kan ƙafafu uku. Sa'an nan idan sasanninsu suka faɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da mai wadar zuci da mai bara. Kamar haka Muka hore muku su, tsammaninku kuna godewa |
Abubakar Mahmoud Gumi Kuma rãƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibãdõjin Allah. Kunã da wani alhẽri babba a cikinsu. Sai ku ambaci sũnan Allah a kansu sunã tsaye a kan ƙafãfu uku. Sa'an nan idan sãsanninsu suka fãɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da mai wadar zũci da mai bara. Kamar haka Muka hõre muku su, tsammãninku kunã gõdẽwa |