×

Surah Ar-Rahman in Hausa

Quran Hausa ⮕ Surah Rahman

Translation of the Meanings of Surah Rahman in Hausa - الهوسا

The Quran in Hausa - Surah Rahman translated into Hausa, Surah Ar-Rahman in Hausa. We provide accurate translation of Surah Rahman in Hausa - الهوسا, Verses 78 - Surah Number 55 - Page 531.

بسم الله الرحمن الرحيم

الرَّحْمَٰنُ (1)
(Allah) Mai rahama
عَلَّمَ الْقُرْآنَ (2)
Yã sanar da Alƙur'ani
خَلَقَ الْإِنسَانَ (3)
Yã halitta mutum
عَلَّمَهُ الْبَيَانَ (4)
Yã sanar da shi bayãni (magana)
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ (5)
Rãnã da watã a kan lissãfi suke
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِ (6)
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَ (7)
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli
أَلَّا تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِ (8)
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَ (9)
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin
وَالْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ (10)
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الْأَكْمَامِ (11)
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُ (12)
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (13)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku *kuke ƙaryatãwa
خَلَقَ الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِ (14)
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ (15)
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (16)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِ (17)
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (18)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ (19)
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ (20)
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (21)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُ (22)
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (23)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالْأَعْلَامِ (24)
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (25)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ (26)
Dukkan wanda ke kanta* mai ƙãrẽwa ne
وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ (27)
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (28)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍ (29)
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (30)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلَانِ (31)
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ *mãsu nauyin halitta biyu
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (32)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالْإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ فَانفُذُوا ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَانٍ (33)
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (34)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ (35)
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (36)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِ (37)
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (38)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلَا جَانٌّ (39)
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (40)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالْأَقْدَامِ (41)
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (42)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
هَٰذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَ (43)
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍ (44)
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (45)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِ (46)
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (47)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
ذَوَاتَا أَفْنَانٍ (48)
Mãsu rassan itãce
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (49)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ (50)
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (51)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِ (52)
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (53)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ ۚ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍ (54)
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (55)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ (56)
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (57)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُ (58)
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (59)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
هَلْ جَزَاءُ الْإِحْسَانِ إِلَّا الْإِحْسَانُ (60)
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (61)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ (62)
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (63)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
مُدْهَامَّتَانِ (64)
Mãsu duhun inuwa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (65)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِ (66)
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (67)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌ (68)
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (69)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌ (70)
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyawun hãlãye, mãsu kyaun halitta
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (71)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِ (72)
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (73)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلَا جَانٌّ (74)
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (75)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
مُتَّكِئِينَ عَلَىٰ رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍ (76)
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa
فَبِأَيِّ آلَاءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ (77)
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلَالِ وَالْإِكْرَامِ (78)
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka
❮ Previous Next ❯

Surahs from Quran :

1- Fatiha2- Baqarah
3- Al Imran4- Nisa
5- Maidah6- Anam
7- Araf8- Anfal
9- Tawbah10- Yunus
11- Hud12- Yusuf
13- Raad14- Ibrahim
15- Hijr16- Nahl
17- Al Isra18- Kahf
19- Maryam20- TaHa
21- Anbiya22- Hajj
23- Muminun24- An Nur
25- Furqan26- Shuara
27- Naml28- Qasas
29- Ankabut30- Rum
31- Luqman32- Sajdah
33- Ahzab34- Saba
35- Fatir36- Yasin
37- Assaaffat38- Sad
39- Zumar40- Ghafir
41- Fussilat42- shura
43- Zukhruf44- Ad Dukhaan
45- Jathiyah46- Ahqaf
47- Muhammad48- Al Fath
49- Hujurat50- Qaf
51- zariyat52- Tur
53- Najm54- Al Qamar
55- Rahman56- Waqiah
57- Hadid58- Mujadilah
59- Al Hashr60- Mumtahina
61- Saff62- Jumuah
63- Munafiqun64- Taghabun
65- Talaq66- Tahrim
67- Mulk68- Qalam
69- Al-Haqqah70- Maarij
71- Nuh72- Jinn
73- Muzammil74- Muddathir
75- Qiyamah76- Insan
77- Mursalat78- An Naba
79- Naziat80- Abasa
81- Takwir82- Infitar
83- Mutaffifin84- Inshiqaq
85- Buruj86- Tariq
87- Al Ala88- Ghashiya
89- Fajr90- Al Balad
91- Shams92- Lail
93- Duha94- Sharh
95- Tin96- Al Alaq
97- Qadr98- Bayyinah
99- Zalzalah100- Adiyat
101- Qariah102- Takathur
103- Al Asr104- Humazah
105- Al Fil106- Quraysh
107- Maun108- Kawthar
109- Kafirun110- Nasr
111- Masad112- Ikhlas
113- Falaq114- An Nas