| وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ (1) Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa
 | 
| الَّذِينَ إِذَا اكْتَالُوا عَلَى النَّاسِ يَسْتَوْفُونَ (2) Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu
 | 
| وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ (3) Kuma idan sun auna musu da zakka* ko da sikẽli, suna ragẽwa
 | 
| أَلَا يَظُنُّ أُولَٰئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ (4) Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba
 | 
| لِيَوْمٍ عَظِيمٍ (5) Domin yini mai girma
 | 
| يَوْمَ يَقُومُ النَّاسُ لِرَبِّ الْعَالَمِينَ (6) Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta
 | 
| كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٍ (7) Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn
 | 
| وَمَا أَدْرَاكَ مَا سِجِّينٌ (8) Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn
 | 
| كِتَابٌ مَّرْقُومٌ (9) Wani ittãfi ne rubũtacce
 | 
| وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ (10) Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa
 | 
| الَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ الدِّينِ (11) Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako
 | 
| وَمَا يُكَذِّبُ بِهِ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ (12) Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi
 | 
| إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ آيَاتُنَا قَالَ أَسَاطِيرُ الْأَوَّلِينَ (13) Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne
 | 
| كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ (14) A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu
 | 
| كَلَّا إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ (15) A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne
 | 
| ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُو الْجَحِيمِ (16) Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne
 | 
| ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ (17) Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi
 | 
| كَلَّا إِنَّ كِتَابَ الْأَبْرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ (18) A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna
 | 
| وَمَا أَدْرَاكَ مَا عِلِّيُّونَ (19) Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna
 | 
| كِتَابٌ مَّرْقُومٌ (20) Wani littãfi ne rubũtacce
 | 
| يَشْهَدُهُ الْمُقَرَّبُونَ (21) Muƙarrabai* suke halarta shi
 | 
| إِنَّ الْأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍ (22) Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima
 | 
| عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ (23) A kan karagu, suna ta kallo
 | 
| تَعْرِفُ فِي وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ النَّعِيمِ (24) Kana sani a cikin fuskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima
 | 
| يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ (25) Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta
 | 
| خِتَامُهُ مِسْكٌ ۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ الْمُتَنَافِسُونَ (26) ¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma
 | 
| وَمِزَاجُهُ مِن تَسْنِيمٍ (27) Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake
 | 
| عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا الْمُقَرَّبُونَ (28) (Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi
 | 
| إِنَّ الَّذِينَ أَجْرَمُوا كَانُوا مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا يَضْحَكُونَ (29) Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya
 | 
| وَإِذَا مَرُّوا بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ (30) Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe
 | 
| وَإِذَا انقَلَبُوا إِلَىٰ أَهْلِهِمُ انقَلَبُوا فَكِهِينَ (31) Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci
 | 
| وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوا إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَضَالُّونَ (32) Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne
 | 
| وَمَا أُرْسِلُوا عَلَيْهِمْ حَافِظِينَ (33) Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu
 | 
| فَالْيَوْمَ الَّذِينَ آمَنُوا مِنَ الْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ (34) To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya
 | 
| عَلَى الْأَرَائِكِ يَنظُرُونَ (35) A kan karagu, suna ta kallo
 | 
| هَلْ ثُوِّبَ الْكُفَّارُ مَا كَانُوا يَفْعَلُونَ (36) Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa
 |