| وَالصَّافَّاتِ صَفًّا (1) Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi)
 | 
| فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًا (2) Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi
 | 
| فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًا (3) Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa
 | 
| إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَاحِدٌ (4) Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne
 | 
| رَّبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِ (5) Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã
 | 
| إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِ (6) Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri
 | 
| وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍ (7) Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai
 | 
| لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلَإِ الْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ (8) Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe
 | 
| دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ (9) Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya
 | 
| إِلَّا مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌ (10) Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi
 | 
| فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا ۚ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍ (11) Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri
 | 
| بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ (12) Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili
 | 
| وَإِذَا ذُكِّرُوا لَا يَذْكُرُونَ (13) Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa
 | 
| وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَ (14) Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili
 | 
| وَقَالُوا إِنْ هَٰذَا إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ (15) Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne
 | 
| أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَبْعُوثُونَ (16) Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne
 | 
| أَوَآبَاؤُنَا الْأَوَّلُونَ (17) Ashe kõ da ubanninmu na farko
 | 
| قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَ (18) Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu
 | 
| فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ (19) Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi
 | 
| وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ الدِّينِ (20) Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako
 | 
| هَٰذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُم بِهِ تُكَذِّبُونَ (21) Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa
 | 
| ۞ احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَ (22) Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa
 | 
| مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَاطِ الْجَحِيمِ (23) Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm
 | 
| وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَ (24) Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne
 | 
| مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ (25) Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna
 | 
| بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ (26) Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne
 | 
| وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ (27) Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna
 | 
| قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِ (28) Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)
 | 
| قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَ (29) Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba
 | 
| وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَ (30) Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka
 | 
| فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا ۖ إِنَّا لَذَائِقُونَ (31) Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne
 | 
| فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَ (32) Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu
 | 
| فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ (33) To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar
 | 
| إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَ (34) Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi
 | 
| إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَٰهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ (35) Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai
 | 
| وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُو آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍ (36) Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci
 | 
| بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَ (37) Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni
 | 
| إِنَّكُمْ لَذَائِقُو الْعَذَابِ الْأَلِيمِ (38) Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne
 | 
| وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ (39) Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa
 | 
| إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ (40) Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
 | 
| أُولَٰئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ (41) Waɗannan sunã da abinci sananne
 | 
| فَوَاكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ (42) Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa
 | 
| فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِ (43) A cikin gidãjen Aljannar ni'ima
 | 
| عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ (44) A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna
 | 
| يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ (45) Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari
 | 
| بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَ (46) Farã mai dãɗi ga mashãyan
 | 
| لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ (47) A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba
 | 
| وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌ (48) Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu
 | 
| كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ (49) Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye
 | 
| فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَ (50) Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna
 | 
| قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌ (51) Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)
 | 
| يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنَ الْمُصَدِّقِينَ (52) Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne
 | 
| أَإِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَإِنَّا لَمَدِينُونَ (53) Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne
 | 
| قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ (54) (Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)
 | 
| فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاءِ الْجَحِيمِ (55) Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim
 | 
| قَالَ تَاللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ (56) Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni
 | 
| وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَ (57) Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)
 | 
| أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ (58) Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba
 | 
| إِلَّا مَوْتَتَنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ (59) Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba
 | 
| إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ (60) Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma
 | 
| لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ الْعَامِلُونَ (61) Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa
 | 
| أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِ (62) Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm
 | 
| إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَ (63) Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai
 | 
| إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِ (64) Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm
 | 
| طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُءُوسُ الشَّيَاطِينِ (65) Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne
 | 
| فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِئُونَ مِنْهَا الْبُطُونَ (66) To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta
 | 
| ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ (67) Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi
 | 
| ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى الْجَحِيمِ (68) Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take
 | 
| إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَ (69) Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu
 | 
| فَهُمْ عَلَىٰ آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَ (70) Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa
 | 
| وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الْأَوَّلِينَ (71) Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu
 | 
| وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ (72) Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu
 | 
| فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَ (73) Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance
 | 
| إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ (74) Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
 | 
| وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَ (75) Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu
 | 
| وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ (76) Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba
 | 
| وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمُ الْبَاقِينَ (77) Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa
 | 
| وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ (78) Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe
 | 
| سَلَامٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَ (79) Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu
 | 
| إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ (80) Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
 | 
| إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ (81) Lalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai
 | 
| ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ (82) Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu
 | 
| ۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَ (83) Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake
 | 
| إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ (84) A lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya
 | 
| إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَ (85) A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa
 | 
| أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَ (86) Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa
 | 
| فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ (87) To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu
 | 
| فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِ (88) Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri
 | 
| فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌ (89) Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne
 | 
| فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَ (90) Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya
 | 
| فَرَاغَ إِلَىٰ آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ (91) Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba
 | 
| مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ (92) Me ya sãme ku, bã ku magana
 | 
| فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِ (93) Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma
 | 
| فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَ (94) Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa
 | 
| قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ (95) Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa
 | 
| وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ (96) Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa
 | 
| قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِ (97) Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm
 | 
| فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الْأَسْفَلِينَ (98) Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci
 | 
| وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهْدِينِ (99) Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni
 | 
| رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَ (100) Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne
 | 
| فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلَامٍ حَلِيمٍ (101) Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri
 | 
| فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَىٰ فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَىٰ ۚ قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ ۖ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَ (102) To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri
 | 
| فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِ (103) Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago
 | 
| وَنَادَيْنَاهُ أَن يَا إِبْرَاهِيمُ (104) Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm
 | 
| قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا ۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ (105) Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
 | 
| إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ الْبَلَاءُ الْمُبِينُ (106) Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna
 | 
| وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ (107) Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma
 | 
| وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ (108) Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe
 | 
| سَلَامٌ عَلَىٰ إِبْرَاهِيمَ (109) Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm
 | 
| كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ (110) Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
 | 
| إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ (111) Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai
 | 
| وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَ (112) Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne
 | 
| وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰ إِسْحَاقَ ۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌ (113) Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin)
 | 
| وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ (114) Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna
 | 
| وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِ (115) Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma
 | 
| وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ (116) Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya
 | 
| وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَ (117) Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni
 | 
| وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَ (118) Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya
 | 
| وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الْآخِرِينَ (119) Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe
 | 
| سَلَامٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَارُونَ (120) Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna
 | 
| إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ (121) Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
 | 
| إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ (122) Lalle, sunã daga bãyin Mu mũminai
 | 
| وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ (123) Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
 | 
| إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلَا تَتَّقُونَ (124) A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba
 | 
| أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَ (125) Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta
 | 
| اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ (126) Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko
 | 
| فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ (127) Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã)
 | 
| إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ (128) Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
 | 
| وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الْآخِرِينَ (129) Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe
 | 
| سَلَامٌ عَلَىٰ إِلْ يَاسِينَ (130) Aminci ya tabbata ga Ilyãs
 | 
| إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَ (131) Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa
 | 
| إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَ (132) Lalle shĩ, yanã daga bãyin Mu mũminai
 | 
| وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَ (133) Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
 | 
| إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ (134) A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya
 | 
| إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ (135) Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba)
 | 
| ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ (136) Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen
 | 
| وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ (137) Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci
 | 
| وَبِاللَّيْلِ ۗ أَفَلَا تَعْقِلُونَ (138) Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba
 | 
| وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَ (139) Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni
 | 
| إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ (140) A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi
 | 
| فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ الْمُدْحَضِينَ (141) Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya
 | 
| فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ (142) Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi
 | 
| فَلَوْلَا أَنَّهُ كَانَ مِنَ الْمُسَبِّحِينَ (143) To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba
 | 
| لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ (144) Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su
 | 
| ۞ فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌ (145) Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya
 | 
| وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ (146) Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi
 | 
| وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ (147) Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka)
 | 
| فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَىٰ حِينٍ (148) Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci
 | 
| فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَ (149) Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza
 | 
| أَمْ خَلَقْنَا الْمَلَائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَ (150) Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce
 | 
| أَلَا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ (151) To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa
 | 
| وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَ (152) Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne
 | 
| أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَ (153) Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza
 | 
| مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ (154) Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)
 | 
| أَفَلَا تَذَكَّرُونَ (155) Shin, bã ku tunãni
 | 
| أَمْ لَكُمْ سُلْطَانٌ مُّبِينٌ (156) Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne
 | 
| فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ (157) To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya
 | 
| وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا ۚ وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ (158) Kuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã)
 | 
| سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ (159) Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa
 | 
| إِلَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ (160) Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
 | 
| فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ (161) To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa
 | 
| مَا أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَاتِنِينَ (162) Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi
 | 
| إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِ (163) Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm
 | 
| وَمَا مِنَّا إِلَّا لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ (164) Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne
 | 
| وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَ (165) Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)
 | 
| وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَ (166) Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi
 | 
| وَإِن كَانُوا لَيَقُولُونَ (167) Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa
 | 
| لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ الْأَوَّلِينَ (168) Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko
 | 
| لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَ (169) Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake
 | 
| فَكَفَرُوا بِهِ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ (170) Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani
 | 
| وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَ (171) Kuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni
 | 
| إِنَّهُمْ لَهُمُ الْمَنصُورُونَ (172) Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako
 | 
| وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَ (173) Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya
 | 
| فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ (174) Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci
 | 
| وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ (175) Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani
 | 
| أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ (176) Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa
 | 
| فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَ (177) To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana
 | 
| وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ (178) Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci
 | 
| وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ (179) Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa
 | 
| سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ (180) Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa
 | 
| وَسَلَامٌ عَلَى الْمُرْسَلِينَ (181) Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni
 | 
| وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ (182) Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu
 |