| لَا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِ (1) Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba
 | 
| وَلَا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِ (2) Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba
 | 
| أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَلَّن نَّجْمَعَ عِظَامَهُ (3) Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba
 | 
| بَلَىٰ قَادِرِينَ عَلَىٰ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُ (4) Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa
 | 
| بَلْ يُرِيدُ الْإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُ (5) Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa
 | 
| يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِ (6) Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma
 | 
| فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُ (7) To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli)
 | 
| وَخَسَفَ الْقَمَرُ (8) Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe)
 | 
| وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ (9) Aka tãra rãnã da watã
 | 
| يَقُولُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّ (10) Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu
 | 
| كَلَّا لَا وَزَرَ (11) A'aha! bãbu mafaka
 | 
| إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّ (12) zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake
 | 
| يُنَبَّأُ الْإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ (13) Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar
 | 
| بَلِ الْإِنسَانُ عَلَىٰ نَفْسِهِ بَصِيرَةٌ (14) Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne
 | 
| وَلَوْ أَلْقَىٰ مَعَاذِيرَهُ (15) Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba)
 | 
| لَا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِ (16) Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni)
 | 
| إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُ (17) Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa
 | 
| فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُ (18) To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa
 | 
| ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُ (19) sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa
 | 
| كَلَّا بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَ (20) A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne
 | 
| وَتَذَرُونَ الْآخِرَةَ (21) Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira)
 | 
| وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ (22) Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne
 | 
| إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ (23) Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne
 | 
| وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌ (24) Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne
 | 
| تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌ (25) Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso
 | 
| كَلَّا إِذَا بَلَغَتِ التَّرَاقِيَ (26) A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai
 | 
| وَقِيلَ مَنْ ۜ رَاقٍ (27) kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada
 | 
| وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُ (28) Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce
 | 
| وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِ (29) Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri
 | 
| إِلَىٰ رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُ (30) Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take
 | 
| فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ (31) To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba
 | 
| وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ (32) Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya
 | 
| ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰ أَهْلِهِ يَتَمَطَّىٰ (33) Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama
 | 
| أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ (34) Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa
 | 
| ثُمَّ أَوْلَىٰ لَكَ فَأَوْلَىٰ (35) Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa
 | 
| أَيَحْسَبُ الْإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًى (36) Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)
 | 
| أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىٰ (37) Bai kasance ɗigo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
 | 
| ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ (38) Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa
 | 
| فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالْأُنثَىٰ (39) Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace
 | 
| أَلَيْسَ ذَٰلِكَ بِقَادِرٍ عَلَىٰ أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىٰ (40) Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu
 |